Shafine da ake bude dan wayar da kan mutane abubuwa wanda zai taimakesu a harkokin yau da kullum, mukan taimaka da abubuwa ta bangaren shawarwari, gyaran jiki, kwalliya da su Girke Girke

A Kama Sana'ar Hannu Domin Kare Mutumcin Kai - Inji Malama Umma Ibrahim

A Kama Sana'ar Hannu Domin Kare Mutumcin Kai - Inji Malama Umma Ibrahim
Umma Ibrahim Adam, ta ce ta shafe shekaru kimanin 20 tana sana’ar sakar kayan sanyin yara, a wani yunkurin zama mai dogaro da kai tare da kawar da kananan bukatu tun tana kuruciya.
Umma ta bayyana cewa ta koyi harkar saka ne a wajen yayarta tun tana karama, daga bisani ta koma makaranta inda ta karanci harshen Arabic ta kuma sami takardarta ta Diploma.
Ta kara da cewa bayan kammala karatunta ta kuma sami aiki koda shike hakan bai sa ta hakura da sana’arta ta saka ba, a cewarta sana’ar na matukar rufa mata asiri inda take kula da marayun da mijinta ya barta da su.
Daga karshe ta bayyana cewa, bata bada bashi, don haka bata samun matsalolin karya jari ko makancin haka, kuma ta koyawa yara matasa da dama harkar saka duk a yunkurin dogaro da kai.


mawallafi:

Shugaban kamfanin Duniyan Fasaha, kuma Babban Editan Mujallar Duniyan Fasaha, mutum ne mai son sanar da mutane abinda Allah ya sanar da shi game da fannoni masu yawa. Mai kokari ne a fannin ilimin, Computer, Web Design, Yanar Gizo, gyaran jiki da sauransu.

No comments:

Post a Comment

TALLA

TALLA

Chanza harshe

Blog Archive

Contact Form

Name

Email *

Message *

Blog Archive