Shafine da ake bude dan wayar da kan mutane abubuwa wanda zai taimakesu a harkokin yau da kullum, mukan taimaka da abubuwa ta bangaren shawarwari, gyaran jiki, kwalliya da su Girke Girke

Nigeria: Osinbajo ya ziyarci garin Numan

Nigeria: Osinbajo ya ziyarci garin Numan
Mataimakin shugaban Nigeria Farfesa Yemi Osinbajo ya ziyarci garin Numan na jihar Adamawa bayan hare-hare da aka kai da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.
Farfesa Osinbajo ya wallafa a shafin sa na Twitter cewa ya ziyarci garin ne don jajantawa al'umma a madadin shugaba Muhammadu Buhari.
Mataimakin shugaban kasar ya ce a tattaunawar da ya yi da masu ruwa da tsaki a garin ranar Talata, ya jaddada musu cewa babban abun da jama'a ke so shi ne zaman lafiya da ci gaba.

A watan Nuwamban 2017 dai rikici mai nasaba da kabilanci ya barke a yankin tsakanin kabilun Bacama da Fulani inda aka kashe mutane akalla 20.
Hare-hare na baya bayan nan shi ne wanda aka kai ranar Litini inda aka hallaka mutane da dama.
A halin yanzu dai an tsaurara matakan tsaro a yankin bayan da kura ta lafa.


mawallafi:

Shugaban kamfanin Duniyan Fasaha, kuma Babban Editan Mujallar Duniyan Fasaha, mutum ne mai son sanar da mutane abinda Allah ya sanar da shi game da fannoni masu yawa. Mai kokari ne a fannin ilimin, Computer, Web Design, Yanar Gizo, gyaran jiki da sauransu.

No comments:

Post a Comment

TALLA

TALLA

Chanza harshe

Blog Archive

Contact Form

Name

Email *

Message *

Blog Archive