Shafine da ake bude dan wayar da kan mutane abubuwa wanda zai taimakesu a harkokin yau da kullum, mukan taimaka da abubuwa ta bangaren shawarwari, gyaran jiki, kwalliya da su Girke Girke

An Janye Haramcin Da Aka Sanyawa Twitter A Nijeriya

An Janye Haramcin Da Aka Sakawa Twitter A Nijeriya

Idan za’a tuna, fiyar (5) ga watan Yunin shekaran data gabata, gwamnatin Najeriya ta haramta amfani da dandalin twitter wadda ta zarga da taimakawa wajen ta da husuma a cikin kasar.

Ko da yake, dakatar da shafin ya biyo ne bayan goge wani sako da shafin Twitter tayi na Shugaba Buhari.

Wata sanarwa data fito daga wajen mai taimakawa shugaba Muhammadu Buhari a fannin kafofin yada labarai na zamani wato Bashir Ahmad yace, gwamnati ta dauki wannan mataki ne bayan da Buhari ya amince.

A cewar Bashir Ahmad, Shugaban kwamitin sasanta tsakanin kasa Najeriya da kamfanin Twitter wadda shi ne shugaban hukumar NITDA na kasa, Kashifu Inuwa ne ya sanar da wannan sabon mataki.

Karanta: Shugaban Twitter ya yimurabus saboda matsin lamba

Haka zalika Twitter ta amince ta hada kai da kasa Najeriya don a yaki mutanen da ke amfani da kafafensu don jawo kiyayya, kyamar juna, rabe-raben kawuna, fitina, addini, kabilanci da kuma kawo tashin hankali a kasar Najeriya baki daya." cewar Garba Shehu.

Bugu da kari Malam Garba Shehu ya ce daga yanzu kamfanin Twitter za ta rika biyan haraji kamar yadda suke biya a kasashen Turai ga kasa Nigeria.

Karanta: Yadda Ake Duba Sakamakon Jarabawar Jamb Na Shekaran Dubu Biyu Da Sha Tara 2019

Ya kara da cewar irin arzikin da kamfanin sada zumuntar Twitter ya samu a Najeriya ya dace a ce yana biyan kudaden haraji masu yawa, .



mawallafi:

Shugaban kamfanin Duniyan Fasaha, kuma Babban Editan Mujallar Duniyan Fasaha, mutum ne mai son sanar da mutane abinda Allah ya sanar da shi game da fannoni masu yawa. Mai kokari ne a fannin ilimin, Computer, Web Design, Yanar Gizo, gyaran jiki da sauransu.

No comments:

Post a Comment

TALLA

TALLA

Chanza harshe

Contact Form

Name

Email *

Message *